Labarai
Sojoji sun kama wanda ake zargin jagoran ’yan ta’adda ne a Kaduna

Dakarun Operation Fansan Yamma sun kama wani da ake zargin jagoran ’yan ta’adda da wasu mutane biyu da ake zargin abokan hulɗarsa ne a Ƙaramar Hukumar Kubau ta Jihar Kaduna.
Rundunar ta ce a wani samame na daban a Ƙaramar Hukumar Igabi, an kama wata mata mai shekaru 50 tana jigilar harsasai 300 da ake zargin za a kai wa ’yan ta’adda a Birnin Gwari.
Sojojin sun kuma kama wani da ake zargin mai samar wa ’yan ta’adda kayan aiki ne, tare da ƙwato na’urorin sadarwa guda huɗu da ake kyautata zaton suna da alaƙa da ayyukan ta’addanci.
An tsare waɗanda ake zargin tare da kayan da aka ƙwato domin ci gaba da bincike da gano sauran mutanen da ke cikin wannan hanyar sadarwa.
You must be logged in to post a comment Login