Labarai
Iran ta sanar da sake rufe mashigar ruwa ta Hormuz

Iran ta sanar da sake rufe mashigar ruwa ta Hormuz bayan musayar sabbin hare-haren su da Amurka.
Amurka ta ce ta kai hare-hare kan muhimman wuraren sojin Iran domin rage ƙarfin sojojinta.
A nata ɓangaren, Iran ta ce ta kai hare-hare kan wuraren da ke da alaƙa da sojojin Amurka a wasu ƙasashen yankin Gulf.
Rikicin ya kuma shafi wasu ƙasashen yankin, ciki har da Qatar, HDL, Kuwait da Oman.
Masana na gargadin cewa rikicin na iya ƙara dagula kasuwannin makamashi, saboda mashigar Hormuz na daga cikin manyan hanyoyin safarar danyen mai a duniya.
You must be logged in to post a comment Login