Connect with us

Labarai

Iran ta kai hare-hare a yankin mashigar Hormuz- Trump

Published

on

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce, Iran ta kai wasu ƙananan hare-hare a yankin mashigin Hormuz, amma bai haifar da babbar illa ga jiragen ruwa ba.

 

Ya kuma ce Amurka na ci gaba da aikin tsaro domin kare zirga-zirgar jiragen ruwa a yankin.

 

Rahotanni sun nuna cewa dakarun Amurka sun lalata wasu ƙananan jiragen ruwan sojin Iran tare da dakile harin makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuƙa da aka kai wa jiragen ruwa na soja da na kasuwanci.

 

Sai dai Iran ta musanta cewa an lalata jiragenta.

 

Iran ta bayyana cewa ta yi harbin gargadi ne kawai a kusa da jiragen ruwan Amurka da ke wucewa a yankin.

 

Wannan rikici ya ƙara tayar da hankali a yankin Gabas ta Tsakiya, musamman saboda muhimmancin mashigin Hormuz wajen jigilar man fetur da iskar gas a duniya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!