Connect with us

Ƙetare

Iran ta yi barazanar rufe mashigar Hormuz baki daya

Published

on

Sakataren Majalisar Tsaron Ƙasa ta Iran, Ali Akbar Zolghadr, ya ce Iran za ta rufe mashigar ruwa ta Hormuz idan Amurka ta ci gaba da kai hare-hare ko takaita zirga-zirgar jiragen ruwa a yankin.

 

Ya gargaɗi cewa hakan zai iya yin mummunan tasiri ga tattalin arzikin duniya, kasuwar makamashi da kuma Amurka.

 

A lokaci guda, kafofin yaɗa labarai na Iran sun ruwaito cewa Tehran ta shirya wani faɗaɗɗen shiri na mayar da martani idan Amurka ta kai hari.

 

Wani babban jami’in tsaro da ba a bayyana sunansa ba ya ce rahotannin yiwuwar harin Amurka da Isra’ila kan Iran “rashin hankali ne”, yana mai cewa martanin Iran zai haɗa da kai hari kan muhimman cibiyoyin Isra’ila da na makamashin Amurka a yankin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!