Connect with us

Ƙetare

Iran ta tabbatar da sake kai sabbin hare-hare a Kuwait da Jordan

Published

on

Iran ta ci gaba da kai hare-hare kan wurare daban-daban a yankin gabas ta tsakiya, bayan sojojin Amurka sun bayyana cewa sun kai jerin hare-haren sama da suka kai kan Iran cikin daren jiya.

Kuwait ta ce wani makami mai linzami da Iran ta harba ya faɗa kan wani gini a arewacin ƙasar, inda ya kashe mutum ɗaya.

Sojojin Jordan kuwa sun ce sun harbo makamai masu linzami guda biyar da Iran ta harba.

Tun da farko, sojojin Amurka sun ce sun kai hari kan wurare da dama mallakin rundunar juyin-juya-halin Iran wato IRGC, a matsayin martani ga harin makamai masu linzami da Iran ta kai ranar Talata kan wani sansanin sojojin Amurka da ke Jordan.

Kafofin yaɗa labarai na Iran sun ce hare-haren na baya-bayan nan da Amurka ta kai sun kashe mutane uku, ciki har da wani yaro.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!