Labaran Wasanni
Jinya: Francis Uzoho ya dawo fagen wasa
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2020/10/16e2af38ba65e74b0ca2cdd41c1a34ec.jpg)
Mai tsaron gidan kungiyar kwallon kafa ta Najeriya Francis Uzoho ya buga wasa na farko bayan ya shafe sama da shekara daya yana jinya bisa rauni da ya sama a kafarsa.
Uzoho dai ya samu rauni a kafarsa yayin da Najeriya take fafatawa da Brazil a wani wasan sada zumunta a kasar Singapore.
Dan wasan yanzu haka yana taka leda a kungiyar kwallon kafa ta APOEL Nicosia dake kasar Cyprus.
Ya kuma taka rawar gani a wasan farko bayan dawowarsa da kungiyar ta yi nasara kan PAEEK da ci uku da nema a gasar Cypriot Cup.
You must be logged in to post a comment Login