Labarai
Kaduna: Rundunar Ƴan sanda ta yi martani kan kisan Ummulkhairi

Rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna ta musanta rahotannin da ke cewa DPO na Marabar Jos, ASP Abdullahi S. Fakai, ya miƙa wata mata mai suna Ummulkairi da ake zargi da satar ƙananan yara ga wasu fusatattun matasa da suka kona ta.
Mai magana da yawun rundunar, DSP Mansur Hassan, ya bayyana cewa jami’an ’yan sanda ne suka fara ceto matar daga hannun jama’a, kuma sun yi iya ƙoƙarinsu wajen kare rayuwarta kafin lamarin ya munana.
Ya kuma ce, zargin da ake yi wa jami’an ’yan sanda ba gaskiya ba ne, yana mai cewa wasu daga cikin shugabannin al’umma ma sun yi ƙoƙarin taimakawa wajen ceton matar.
DSP Mansur ya ƙara da cewa abin da ya faru ya samo asali ne daga matakin da wasu fusatattun matasa suka ɗauka, yana mai zargin cewa wasu mazauna yankin na ƙoƙarin kau da laifi daga kansu ta hanyar ɗora alhakin kan jami’an tsaro.
Rundunar ta jaddada cewa tana ci gaba da bincike kan lamarin domin gano duk waɗanda ke da hannu a aika-aika tare da tabbatar da an hukunta su bisa tanadi doka.
You must be logged in to post a comment Login