Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kano: Hisbah ta magantu kan rikicin ƴan adaidaita

Published

on

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta yi kira ga al’ummar jihar musamman matasa da su guji tayar da zaune tsaye.

Babban Kwamandan hukumar Malam Haruna Ibn Sina ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labaran hukumar Malam Lawan Ibrahim Fagge ya fitar a daren jiya Litinin.

Malam Ibn Sina ya ce, baki-ɗaya an gina addinin musulunci ne a bisa zaman lafiya.

A don haka ya roƙi al’ummar Kano da su yi duk mai yiwuwa wajen tabbatar da ɗorewar zaman lafiya.

Malam Ibn Sina ya kuma roƙi al’ummar Kano da su ƙara dage wa da addu’ar neman zama lafiya a jihar da ƙasa baki-ɗaya.

Wannan dai na zuwa ne bayan samun rahoton tarzoma a wasu yankunan Kano sanadiyyar zanga-zangar masu adaidaita sahu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!