Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kano: Mutane 167 ne suka kamu cutar fitsarin jini a mako guda

Published

on

Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano ta ce, kawo yanzu mutane 167 ne suka kamu da cutar nan da ta ɓulla a wasu yankunan jihar.

A wata zanta wa da Freedom Radio, Daraktan lura da cutuka na ma’aikatar Dr. Bashir Lawan, ya ce, tuni aka ƙara samar da asibitoci guda takwas domin lura da waɗanda suka kamu da cutar, wadda ya ce ana zargin tana da alaƙa da guba.

Asibitocin sun haɗa da, Asibitin zana, da asibitin koyarwa na Aminu Kano sai asibitin Ƙwararru na Murtala.

Sauran su ne asibitin Waziri Shehu Giɗaɗo, da kuma asibitin Sheikh Jidda da kuma babban asibitin garin Rano da wasu asibitoci biyu a ƙaramar hukumar Dawakin Tofa.

Dr. Bashir ya ƙara da cewa, yanzu haka cutar ta mamayi ƙananan hukumomi takwas da suka haɗa da ƙaramar hukumar Gwale da Birnin da Kewaye.

Sauran su ne ƙananan hukumomin Dala da kuma Fagge da Bunkure, sai Dawakin Tofa da Gwarzo.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!