Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kano: Red Cross ta yi tsokaci kan Coronavirus

Published

on

Kungiyar bada agajin gaggawa ta RED CROSS tayi kira ga al’ummar kasar nan dasu kara kaimi wajen kula da tsaftar muhallin su domin kare kansu daga kamuwa da cutar Coronavirus da cutar Lassa.

Jami’in kula da lafiya na kungiyar bada agajin gaggawa ta Red Cross reshen jihar Kano Salisu Garba Ahmad ne ya bayyana hakan, lokacin taron wayar da kai da kungiyar dake rajin samarda ayyukan yi da hadin gwiwar gidauniyar Mailemo suka shirya.

Salisu Garba Ahmad ya kara da cewa matukar mutane basu dauki matakan kare Kansu daga wadannan cututtuka ba musamman wajen tsaftace muhallan su da kuma kaucewa duk wasu hanyoyin da zasu iya kawo cutar ba babu shakka cutar zata cigaba da samun gindin zama a tsakanin mutane.

A nasa jawabin shugaban kungiyar samar da ayyukan yi reshen jihar Kano Abubakar Umar Barkama cewa yayi sun dauki matakin shirya taron ne domin su wayar da kan mutane musamman akan matsalolin da ake fama dasu a bangaren lafiya anan Najeriya.

Wakilin mu Abdulkarim Muhammad Abdulkarim Tukuntawa ya ruwaito cewa wakilan kungiyoyi da dama ne suka halarci taron, inda masana kiwon lafiya suka gudanar da makala kan yadda za a magance matsalar kamuwa da cutar coronavirus da cutar Lassa a Najeriya.

Karin labarai:

Musulmai sun yi taron addu’a kan Coronavirus a Kano

Ganduje : zan yi duk mai yuwa wajen hana COVID-19 shigowa Kano

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!