Connect with us

Labarai

Mambobin NUT sun dakatar da yajin aikin da suke yi a Abuja

Published

on

Kungiyar Malaman makaranta ta kasa NUT reshen Babban Birnin Tarayya Abuja  ta dakatar da yajin aikin malaman firamare da sakandare nan take, bayan taron gaggawa da aka gudanar domin nazarin shiga tsakani da Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya yi a rikicin da ya fara ranar 20 ga Afrilun nan da muke ciki.

 

Shugaban kungiyar, Abdullahi Shafa, ya ce ministan ya amince da ware naira biliyan 5 duk wata domin biyan bukatun malamai, inda biliyan 2 za su fito daga kudaden shiga na Abuja, sannan biliyan 3 daga kaso 10 cikin 100 na kudaden shiga da kananan hukumomi ke samu, domin biyan alawus na musamman na kashi 40 da sauran hakkoki.

 

Kungiyar ta umurci dukkan malamai su koma bakin aiki ranar Litinin 27 ga Afrilu, tare da gargadin cewa kada a hukunta wani malami saboda shiga yajin aikin. Ta kuma ce za ta sake duba matsayarta idan gwamnatin Abuja ba ta cika alkawuran da ta dauka ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!