Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kotu ta bada umarnin tsare Engr Idris Wada Sale a PCACC

Published

on

Kotun Magistrate da ke zamanta a Kano ta sahalewa hukumar karbar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ci gaba da tsare tsohon kwamishinan ayyuka a gwamnatin Ganduje, watau Injiniya Idris Wada Saleh kwanaki 12 masu zuwa, sakamakon zarginsa da almundahanar naira biliyan daya na aikin gyaran wasu tituna.

Mai shari’a Tijjani Sale Minjibir, ne ya ba da umarnin ci gaba da tsare tsohon shugaban hukumar gyaran titunan ta Kano KARMA, a bisa kama shi da kuma gurfanar da shi da hukumar ta Anti-Corruption ta yi.

Da fari dai lauyan hukumar Salisu Tahir, ya roki kotun da ta sahale musu ci gaba da rike tsoho kwamishinan na tsawon kwani 14, yayin da kuma lauyan wanda ake kara Mustafa Idris, ya bukaci kotun da ta ba da belinsa.

Mai shari’a Tijjani Sale Minjibir, ya dage sauraren karar zuwa ranar 14 ga watan nan na  Yuli da muke ciki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!