Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Kotu ta dakatar da jagororin NALCOF reshen jihar Kano

Published

on

Kotun Majistare ƙarkashin mai shari’a Tijjani Saleh Minjibir, mai lamba 60 a gidan Murtala dake Kano ta dakatar da shugabannin ƙungiyar masu ƙungiyoyin ƙwallon kafa rukuni na ɗaya ta ƙasa wato (NALCOF), sakamakon ƙarewar wa’adin su.

Tun da farko wasu mutane huɗu Dauda Auwalu Zage da Aminu Abba Ƙwaru da Auwalu Salisu sai Mu’awiyya Adamu, sun shigar da ƙara tare da neman dakatar da tsagin shugabancin da wa’adin su ya ƙare, kan su bada ikon gudanar da komai da ke hannun su ga shugaban gudanar da zaɓe na sabbin jagororin ƙungiyar.

Waɗanda ake ƙara sun haɗa da, ƙungiyar ta NALCOF, sai Faruk Ibrahim da Aliyu Kassim sai Salisu Ibrahim Danladi da Auwalu Saminu tare da Sani Isyaku Dogo da Salisu Usman sai Muzammil Ɗalha Yola da Shehu Muhammad Yellow da Ujudu Muhammad S/Fada.

Bayan dakatarwar kotun ta umarci waɗanda ake ƙara da su daina nuna kan su a matsayin jagororin ƙungiyar kasancewar hakan ya saɓa ka’ida, sakamakon ƙarewar wa’adin mulkin su tun ranar 5 ga watan Janairun shekarar 2015.

Kotun ta ɗage zaman sauraron shari’ar har zuwa ranar 9 ga watan Oktoba mai zuwa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!