Labarai
Kotu ta hana Hukumar NBC hukunta ƴan jarida kan bayyana ra’ayinsu

Babbar kotun tarayya da ke Legas ta hana hukumar kula da kafafen yaɗa labarai ta Nijeriya wato NBC, da amfani da sanarwar da ta fitar ta gargaɗi kan hukunta masu gabatar da shirye-shirye da kafafen yaɗa labarai daga bayyana ra’ayinsu.
Mai shari’a Daniel Osiagor ne ya bayar da umarnin wucin gadi na hana aiwatar da hakan a ranar Litinin, bayan sauraron hujjojin da aka gabatar a wata shari’ar gaggawa da ƙungiyar SERAP da kuma ƙungiyar manyan Editocin Nijeriya suka shigar.
You must be logged in to post a comment Login