Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Koyi da bakin al’adu shi ke kawo mutuwar aure a Najeriya

Published

on

Shugaban cibiyar wayar da kan al’umma da karfafa musu gwiwa kan zamantakewa malam Auwal Salisu ya ce rashin bin koyarwar addinin islama da bijirewa al’adun bahaushe da koyi da bakin al’adu na bayar da gudunmuwa wajen tabarbarewar aure.

Malam Auwal Salisu ya bayyana hakan ne jim kadan bayan kammala shirin barka da hantsi na Freedom radio wanda ya mayar da hankali kan taron da cibiyar ta gudanar a ranar asabar din da ta gabata don wayar da kan al’umma kan zamantakewar aure.

Shugaban ya kuma kara da cewar babban abinda ke kawo mutuwar aure a wannnan lokaci rashin gina aure akan gaskiya wanda hakan shine ke haifar da matsalar.

A nasa bangaren Malam Tijjani Muhammad Musa ya bayyana cewar iyaye na taka muhimmiyar rawa wajen tabarbarewar aure da rashin dora yaransu hanyar da ta dace.

Tijjani Muhammad Musa ya kara da cewar duk wanda suka kasance miji da mata su sauke girman kai da wasu dabi’u wanda suke kara kawo matsala a zamantakewa.

Bakin sun kuma bukaci iyaye su kasance masu koyawa ‘ya’yan su ilimin zamantakewar aure kafin aurar da su tare da nusar dasu hanyoyin da zasu girmama junan su a matsayin ma’aurata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!