Connect with us

Labarai

Kwamitin majalisar wakilai zai gurfanar da babban Akanatan Najeriya

Published

on

Kwamitin da ke binciken kafa hukumar Bogi na majalisar wakilai zai gurfanar da babban Akanatan kasar nan Mista Shamsedeen Ogunjimi, a yau domin yi masa tambayoyi dangane da yadda aka fitarwa da hukumar kudi.

Kwamitin, karkashin jagorancin dan majalisa mai wakiltar kananan hukumomin Kanke, Kanam da Pankshin a Jihar Filato, Yusuf Gagdi, na binciken yadda hukumar Bogin ta samu ofis a harabar Babbar Sakatariyar Gwamnati da ke Abuja, tare da samun fiye da Naira biliyan Daya a cikin kasafin kudin shekarar 2026.

Binciken ya jawo hankalin jama’a bayan zargin cewa hukumar ta gudanar da ayyuka a cikin tsarin gwamnati duk da rashin sahihancin ta, lamarin da ya haifar da tambayoyi kan yadda ake tafiyar da kudaden gwamnati da kuma tsarin sa ido kan hukumomi.

Ana sa ran Akanta Janar zai yi bayani kan yadda hukumar ta samu lambar kasafi wato (budget code), wadda ta ba ta damar shiga cikin kasafin kudin kasa duk da cece-kuce kan matsayinta a doka

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!