Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ma’aikatan man fetur sun yi barazanar shiga yajin aiki a Najeriya

Published

on

Gamayyar kungiyoyin Ma’aikatan Man Fetur da na iskar Gas ta Najeriya sun yi barazanar shiga yajin aiki, a cikin wata wasika da suka aikewa ministan Man Fetur, Timipre Sylva.

Najeriya na iya fuskantar matsalar karancin mai idan ma’aikatan suka kauracewa aiyukan su yayinda gwamnatin kasar ta dage kan yiwa ma’aikata a bangaren mai rijista a kan hadaden sabon tsarin albashi da ta bullowa ma’aikatan da ke aiki a wurare daban-daban wato IPPIS

Kamar yadda rahotanni suka tabbatar gamayyar kungiyoyin ma’aikatan sun nuna adawarsu karara ga matakin ofishin akanta janar na tarayya game da rijistar ma’aikatan man fetur din a kan tsarin IPPIS.

Cikin wasikar da suka aikewa ministan man fetur mai dauke da kwanan watan 19 ga watan Yunin 2020, na dauke da sa hannun manyan shugabannin kungiyoyin PENGASSAN da NUPENG, wato Lumumgba Okugbawa da Olawale Afolabi.

Kungiyoyin sun tabbatar da cewa za su tsunduma yajin aiki, matsawar gwamnati ta gaza daukar mataki a kan bukatunsu.

Kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito, kungoyin basu bayyana ranar da zasu shiga yajin aikin ba, sai dai suna da yakinin gwamnatin zata duba bukatunsu domin kaucewa matsalar da Najeriya ka iya fadawa game da matsalar man fetur din.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!