Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mahaddatan alƙur’ani sun goyi bayan Ganduje kan hana bara

Published

on

Ƙungiyar mahaddatan alƙur’ani ta ƙasa ta ce za ta tabbatar da hana barace-barace a tsakanin almajirai.

Shugaban ƙungiyar Gwani Aliyu Salihu Turaki ne ya bayyana hakan yayin ziyarar da suka kai wa gwamnan Kano.

Gwani Aliyu ya ce, za su tsaya kai da fata wajen tabbatar da ƙara inganta makarantun tsangayu a Kano.

Labarai masu alaka:

Dalilan da suka sanya Ganduje ya hana bara a Kano – Dr. Sa’idu Dukawa

Ganduje zai fara kwashe almajirai dake barace-barace akan tituna

Shi kuwa Gwamna Abdullahi Umar Ganduje cewa ya yi, gwamnatinsa ba ta da burin hana karatun tsangaya.

Hassalima tana da shirye-shirye na musamman domin ƙara inganta tsarin karatun.

Gwamna Ganduje ya ce, gwamnatinsa za ta ƙara jajircewa wajen ganin an daƙile bara domin tana haifar da illa ga almajirai.

Ku kalli hotunan ziyarar da kungiyar ta kai wa gwamnan

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!