Labarai
Shugaan APC Nentawe ya soki shirin Atiku na tallafin mai

Shugaban jam’iyyar APC na kasa Farfesa Nentawe Yilwatda, ya ce shirin Atiku Abubakar na mayar da tallafin man fetur na iya jefa Najeriya cikin matsin tattalin arziki.
Yilwatda ya ce matakin na iya sa ƙasar ta koma cikin matsalolin tattalin arziki da ta fara fita daga ciki.
Shugaban ya bayyana hakan ne yayin da ake ci gaba da muhawara kan cire tallafin man fetur da kuma yadda za a rage wa ’yan Najeriya wahalhalun rayuwa.
Sai dai magoya bayan Atiku na ganin cewa dawo da tallafin zai taimaka wajen rage tsadar man fetur da kuma sauƙaƙa wa ’yan Najeriya halin da suke ciki.
You must be logged in to post a comment Login