Labarai
Majalisar Dattawa ta kare matakin ta na amincewa da kafa yan sandan jihohi

Majalisar Dattawan Najeriya ta kare matakin da ta ɗauka na amincewa da kudirin gyaran kundin tsarin mulki na kafa rundunar ‘yan sandan jihohi, in da ta ce batun tsaron ƙasa ya kamata ya fi duk wata siyasa muhimmanci.
Shugaban masu rinjaye na Majalisar Dattawa, Sanata Opeyemi Bamidele, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, bayan wasu ‘yan siyasa sun nuna adawa da aiwatar da tsarin.
A makon da ya gabata ne Majalisar Dattawa ta amince da kudirin da ke neman kafa rundunar ‘yan sandan jihohi a faɗin ƙasar nan, lamarin da ya sha suka daga bangarorin adawa da wasu jama’a.
You must be logged in to post a comment Login