Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Manchester City ta lashe gasar firimiyar ƙasar Ingila

Published

on

Manchester City ta lashe gasar firimiyar ƙasar Ingila bayan da ta samu nasara a kan Aston Villa da ci 3-2 a wasan ƙarshe na gasar.

Manchester City ta ɗauki gasar ta shekarar 2021/2022 a yau Lahadi 22/5/2022, bayan buga wasanni 38 na gasar.

Tun a mintuna na 37 ƙungiyar Aston Villa ta shiga gaban Manchester City bayan da ɗan wasan ta Matty Cash ya zura ƙwallon farko, sai kuma a mintuna na 69 ɗan wasa Philip Coutinho ya ƙara ƙwallo a ragar Manchester City wanda ya zama jimilla suna da ƙwallo 2.

Sai dai a minti na 76 likay Gundigon na Manchester City ya warware ƙwallon farko kafin daga bisani a mintuna na 78 ɗan wasa Rodry ya warware ƙwallayen 2 da Aston Villa ta zura musu.

A minti na 81 ɗan wasa Likay Gundigon ya ƙarawa ƙungiyar sa ta Manchester City ƙwallo wanda ya zama jimilla Manchester City tana da ƙwallo 3 ita kuma Aston Villa tana da 2.

Kuma da wannan nasara ce yasa Manchester City lashe gasar firimiyar Ingila ta shekarar 2021/2022 da maki 93.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!