Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Masarautar Kano ta yabawa shirin ECOWAS 2020

Published

on

Maimartaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya yaba wa shirin muradan raya tattalin arziƙin ƙasashen Afrika ta yamma na ECOWAS – Vision 2020 zuwa 2050.

Sarkin ya bayyana hakan ne ta bakin Ɗan Malikin Kano Ambasada Ahmed Umar, yayin taron bita da tuntuɓar juna na kwanaki biyu game da shirin, wanda aka gabatar a ranakun jiya Litinin da yau Talata a nan Kano.

Taron dai ya mayar da hankali ne kan sabbin shirye-shiryen da za a samar a shiri na gaba mai taken Vision – 2050.
Bayan kammala taron wakiliyarmu Hassana Salisu Abubakar ta tuntuɓi Ɗan Malikin Kano, wanda ya yi mana ƙarin haske game da yadda taron ya kasance.

Ɗan Malikin na Kano, ya ce, Maimartaba Sarkin Kano ya hori masu shirya shirin da su yi la’akari da jihar Kano duba da yawan albarkatu musamman na kasuwanci da jihar ke da shi.

Haka kuma, Sarkin na Kano ya ce, la’akari da tasirin da cutar Coronavirus ta yi wajen kassara masu sana’o’i akwai buƙatar sabon shirin ya bada fifiko wajen farfaɗo da tattalin arziƙin al’umma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!