Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Masu Corona sun haura 400 a Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta tabbatar da cewa mutane 427 ne suka kamu da cutar Covid-19 a jihar.

Ma’aikatar lafiya ta Kano ta sanar a shafinta na Twitter cewa a ranar Laraba an samu karin mutane 30 da suka kamu da cutar a jihar.

Har ila yau, ma’aikatar lafiyar ta Kano ta ce an samu karin mutane 3 da aka sallama bayan sun warke daga cutar, yanzu haka mutane 6 ne suka warke daga Coronavirus a jihar Kano.

Sanarwar ma’aikatar lafiyan tace an samu karin mutane 5 da suka rasa ransu sanadiyyar cutar ta Corona, wanda ya kai adadin wadanda cutar ta hallaka a jihar zuwa mutane 13.

Karin labarai:

Yadda mutane 3 na farko suka warke daga Corona a Kano

Yadda Likitoci 34 suka kamu da Corona a Kano

Yanzu haka dai mutane 408 ne ke dauke da cutar wadanda suke karbar kulawa daga wurin jami’an lafiya.

Jihar Kano dai ita ce jiha ta biyu a jihohin dake da yawan wadanda suma kamu da cutar ta Covid-19 a kasarnan.

Ko a ranar Talatarnan an tabbatar da cewa likitoci 34 ne suka kamu da cutar ta Covid-19 a jihar ta Kano.

Yayinda a ranar Laraba kuma rahotonni suka tabbatar da cewa ma’aikatan jinya da Ungozoma 18 ne suka kamu da cutar ta Covid-19 a Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!