Connect with us

Labarai

Mun ta fara yin amfani da fasahar zamani wajen tsaron iyakokin Najeriya- NIS

Published

on

Hukumar kula da shige da fice NIS, ta ce ta fara yin amfani da fasahar zamani wajen tsaron iyakokin Najeriya.

Kwanturola Janar ta hukumar, Kemi Nandap, ce ta bayyana hakan a jihar Lagos, yayin wani taro na jami’an da ke kula da iyakokin kasashen Afrika.

Ta ce, hukumar na amfani da tsarin tantance shaidar mutum ta zamani, da na’urorin sarrafa zirga-zirgar mutane ta atomatik da kuma sa ido bisa bayanan sirri, domin karfafa tsaron iyakoki ba tare da hana halastacciyar zirga-zirga da cinikayyar kasashen ketare ba.

Kemi Nandap ta ce ya kamata a daina kallon tsaron da ake baiwa iyakokin kasashe a matsayin hanyar raba kan kasashe.

A cewarta, babban kalubalen gwamnati shi ne tabbatar da tsaron iyakoki tare da tabbatar da cewa matafiya, ‘yan kasuwa da al’ummomin da ke zaune a kan iyakoki ba su fuskanci takura ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!