Labarai
Za mu fitar da rahoto kan kisan mutanen ranar rantsar da mataimakin gwamna da fasa shaguna a Farm Center- Amnesty

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Bil’adama ta Amnesty International ta ce duk ɗan siyasa ko malamin addini da aka samu yana tunzura mutane domin aikata wani abu yayin yaƙin neman zaɓe, wanda hakan zai iya janyo asarar rayuka ko barnatar da dukiyoyi, zai fuskanci hukunci.
Haka zalika, ƙungiyar ta ce nan ba da jimawa ba za ta fitar da rahoto kan kisan mutanen da ya faru a lokacin rantsar da mataimakin gwamnan Kano, da kuma fasa shaguna a kasuwar Farm Center.
Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Isa Sunusi, ne ya bayyana hakan a wata zantawa da Freedom Radio
You must be logged in to post a comment Login