Connect with us

Labarai

Mun taba bincikar Tinubu kan zargin safarar miyagun kwayoyi- FBI

Published

on

Hukumar Bincike ta kasar Amurka FBI, ta tabbatar da cewa Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kasance cikin mutanen da ta gudanar da bincike a kansu bisa laifukan safarar miyagun ƙwayoyi a farkon shekarun 1990.

 

Wannan na cikin wata takardar rantsuwa da hukumar ta gabatar wa wata kotun tarayya a birnin Washington DC, a matsayin wani ɓangare na ƙarar neman bayanan binciken shugaba Tinubu.

 

Sai dai hukuncin kotun bai tabbatar da cewa shugaba Tinubu ya aikata laifin safarar ƙwayoyi ko kuma an taɓa samun hukuncin laifi a kansa ba.

 

Hukumar FBI ta ce, wasu bayanan har yanzu ba za ta bayyana su ba saboda dalilan kare sirri da kuma hanyoyin binciken jami’an tsaro.

 

A nasa martanin, mai bai wa Shugaba Tinubu shawara kan harkokin yaɗa labarai, Sunday Dare, ya yi watsi da batun, ya na zargin cewa ana amfani da tsoffin bayanan Amurka ne domin siyasa gabanin zaɓen 2027 da ke tafe.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!