Connect with us

Labarai

Mutane 16 sun mutu sakamakon yunwa a kasar Uganda

Published

on

Gwamnatin Uganda ta ce aƙalla mutum16 sun mutu sakamakon yunwa a yankin Karamoja da ke arewa maso gabashin ƙasar, bayan dogon fari da ya lalata amfanin gona.

Firaministar Uganda, Robinah Nabbanja, ta ce dubban iyalai sun rasa abinci bayan rashin ruwan sama tun daga watan Afrilu, lokacin da ake fara shuka amfanin gona.

Manoma sun ce gonakin masara, dawa da waken soya sun lalace saboda ƙarancin ruwa, lamarin da ya rusa fatan samun girbi mai yawa a bana.

Gwamnatin ta fara raba kayan agajin gaggawa, yayin da masana ke danganta matsalar da sauyin yanayi, sare itatuwa, yawan kiwo ba tare da kulawa ba da kuma ƙwarin da ke lalata amfanin gona. Sun yi kira da a ƙara zuba jari a ban ruwa da kuma iri masu jure fari.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!