Labarai
Mutane 16 sun mutu sakamakon yunwa a kasar Uganda

Gwamnatin Uganda ta ce aƙalla mutum16 sun mutu sakamakon yunwa a yankin Karamoja da ke arewa maso gabashin ƙasar, bayan dogon fari da ya lalata amfanin gona.
Firaministar Uganda, Robinah Nabbanja, ta ce dubban iyalai sun rasa abinci bayan rashin ruwan sama tun daga watan Afrilu, lokacin da ake fara shuka amfanin gona.
Manoma sun ce gonakin masara, dawa da waken soya sun lalace saboda ƙarancin ruwa, lamarin da ya rusa fatan samun girbi mai yawa a bana.
Gwamnatin ta fara raba kayan agajin gaggawa, yayin da masana ke danganta matsalar da sauyin yanayi, sare itatuwa, yawan kiwo ba tare da kulawa ba da kuma ƙwarin da ke lalata amfanin gona. Sun yi kira da a ƙara zuba jari a ban ruwa da kuma iri masu jure fari.
You must be logged in to post a comment Login