Labarai
NAHCON ta sanar da ranar rufe rajistar maniyyatan 2027

Hukumar kula da aikin hajji ta kasa NAHCON, ta ce saura kwanaki bakwai kacal kafin rufe rajistar masu niyyar zuwa aikin Hajjin shekarar 2027.
Hukumar ta ce wa’adin rajistar da kuma shigar da bayanan mahajjata zai kare ne a ranar 26 ga watan Satumbar da muke ciki.
NAHCON ta kuma bukaci masu niyyar zuwa Hajjin da ba su kammala rajistar su ba, da su gaggauta yin hakan, domin kauce wa rasa damar shiga cikin shirin hajjin na shekarar 2027.
Hukumar ta kuma bukaci mahajjatan da su tabbatar da cewa an shigar da bayanansu yadda ya kamata kafin wa’adin ya cika.
You must be logged in to post a comment Login