Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

NERC ta fayyace yadda farashin lantarki zai kasance

Published

on

Hukumar kula da bangaren samar da wutar lantarki ta kasa NERC ta kara fayyace yadda farashin lantarki zai kasance.

Hukumar ta NERC ta ce karin kudin wuta da aka yi a baya-bayan nan bai shafi muaten da ke samun wuta kasa da awanni goma sha biyu a duk rana ba.

Kwamishina mai kula da harkokin shari’a da ba da lasisi na hukumar Mista Dafe Akpeneye ne ya fayyace hakan yayin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a kafar internet.

A cewar sa, dukkannin abokin huldar kamfanonin rarraba wutar lantarki da basa samun wuta akalla awanni goma sha biyu a rana to basa cikin karin farashin da aka yi.

A ranar daya ga wannan wata na Satumba ne kamfanonin rarraba wutar lantarki suka sanar da sabon tsarin farashin wutar lantarki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!