Labarai
NiMet ta yi hasashen samun tsawa da ruwan sama a jihohi 10 na Arewacin Najeriya

Hukumar hasashen yanayi ta kasa NiMet ta yi hasashen samun tsawa tare da saukar ruwan sama a jihohi 10 na Arewacin kasar da kuma wasu jihohin Kudancin kasar, a yau Lahadi.
Wannan na kunshe ne a cikin hasashen yanayin da hukumar ta fitar a shafinta na X a yammacin jiya Asabar.
Hasashen ya nuna cewa za a samu bullar hasken rana a Arewacin ƙasar a safiyar Lahadi, kuma ranar za ta iya zuwa da zafi, ta ce ana sa ran samun tsawa da ruwan sama a wasu sassa na kudancin jihar Adamawa da Taraba tun da safiyar da ta gabata.
NiMet ta ce za a samu ruwan sama a Abuja da jihohin Nasarawa, Plateau, Benue, Kwara da Kogi a yammacin yau Lahadi.
Ya yin da ta ce a kudancin ƙasar kuwa, yanayin zai kasance mafi tsanani inda za a samu ruwan sama kusan a dukkan jihohin yankin, ciki har da Akwa Ibom, Rivers, Cross River, sai da yammacin ranar za a samu ruwan sama a Lagos, Ogun, Oyo, Osun, Ekiti, Ondo, Edo, Delta, Bayelsa, Rivers, Cross River, Akwa Ibom, Abia, Imo, Anambra, Enugu, Ebonyi.
You must be logged in to post a comment Login