Connect with us

Labarai

Wata ambaliyar ruwa a Jalingo babban birnin jihar Taraba ta yi mummunar barna

Published

on

Ambaliyar ruwa a Jalingo babban birnin jihar Taraba ya yi sanadiyyar  rushewar  gidaje da kuma shafe kadarori da dama. 

 

Rahotanni sun ce ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da aka fara tun ƙarfe 2:30 na dare zuwa 11:30 na safiyar jiya Asabar  ne ya yi sanadin ambaliyar da Rahotanni suka tabbatar da cewa ta shafi unguwannin Mile Six, Mafindi da kuma Mayogwai, sai kuma babbar kasuwar Jalingo da ruwan ya shafe shaguna.

 

Mazauna yankunan da ambaliyar ta fi shafa sun shaidawa manema labarai cewa ta faru ne a sakamakon toshewar magudanan ruwa.

 

Bayanai sun nuna cewa ambaliyar ta kuma haddasa cunkoson ababen hawa a kan babbar hanyar Jalingo zuwa Wukari sakamakon yadda ta haɗu da aikin sabuwar gada da ake ginawa.

 

Wannan shine karo na biyu cikin makonni uku da ruwan sama ke dakatar da aikin ginin gadar.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!