Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ranar daukar hoto: Akwai marasa ƙwarewa a harkar – Ƙungiyanar daukar hoto:

Published

on

Ƙungiyar masu ɗaukar hoto ta ƙasa reshen jihar Kano ta ce, harkar ɗaukar hoto na fuskantar matsala sakamakon shigar waɗanda ba su da ƙwarewa a harkar.

Shugaban ƙungiyar Abdulwahab Sa’id Ahmad ne ya bayyana hakan, jim kaɗan bayan kammala shirin “Barka da Hantsi” na nan Freedom Radiyo, wanda yayi duba kan mahimmanci ranar dauka hoto ta duniya da ake gudanarwa a duk ranar 19 Agusta.

Abdulwahab ya ce, “Babban ƙalubalen ƙungiyar bai wuce yadda ma’ikatun gwamnati ke ƙin ɗaukar ƙwararrun masu ɗaukar hoto don su yi aiki tare da su ba”.

Guda daga cikin membobin kungiyar da ta kasance cikin shirin Hafsa Sani Muhammad ta ce, “Rashin isassun mata a cikin kungiyar koma baya ne a harkar”.

Sai dai ta buƙaci gwmanati da ta riƙa ɗaukar nauyin matasa wajen fitar da su guraren da za su koyi harkar gyaran kyamara musamman ma ta zamani.

 

 

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!