Connect with us

Labarai

Rundunar sojin sama ta kasa ta kashe ’yan ta’addan ISWAP 36

Published

on

Rundunar sojin sama ta kasa ta ce ta kashe ’yan ta’addan ISWAP 36 a wasu hare-haren sama da ta kai a kananan hukumomin Monguno da Biu na Jihar Borno.

 

Jami’in yada labarai na Operation Hadin Kai, Kyaftin Mohammed Goni, ya ce an kai hare-haren ne a dararen Juma’a da Asabar, bayan samun sahihan bayanan sirri da sa ido ta sama.

 

Ya ce a yankin Aduwa na Monguno, an kashe ’yan ta’adda 26 a hare-hare daban-daban, yayin da wasu 10 kuma aka kashe a yankin Buratai na karamar hukumar Biu.

 

Rundunar ta ce hare-haren sun taimaka wajen tarwatsa yunkurin ’yan ta’addan na sake haduwa da kuma gudanar da ayyukansu.

 

Ta kuma ce za a ci gaba da amfani da bayanan sirri da sa ido ta sama domin takaita zirga-zirgar ’yan ta’adda da kuma kara matsin lamba a kansu a yankin Tafkin Chadi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!