Labarai
SERAP ta bukaci ’yan takarar shugaban kasa su bayyana kadarorinsu a bainar jama’a kafin zabe

Kungiyar da ke rajin tabbatar da adalci ta SERAP ta bukaci dukkan ’yan takarar shugaban kasa a zaben 2027, ciki har da shugaba Bola Ahmed Tinubu, Atiku Abubakar da Peter Obi, da su bayyana kadarorinsu a bainar jama’a kafin gudanar da zaben.
SERAP ta ce bayyana kadarorin ’yan takara zai taimaka wajen kara gaskiya da rikon amana a harkokin siyasa, tare da bai wa ’yan Najeriya damar sanin matsayin dukiyar wadanda ke neman shugabancin kasar.
Kungiyar ta kuma ce ya kamata ’yan takarar su guji duk wani nau’in sayen kuri’u, domin tabbatar da zabe mai inganci da adalci.
You must be logged in to post a comment Login