Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Shekaru 25 rabon da Afrika ta Kudu ta lashe kofin Afrika

Published

on

A makamanciyar irin wannan ranar ce ta uku ga watan Fabrairun shekarar 1996 kasar Afrika ta Kudu ta kafa tarihin lashe gasar cin kofin kasashen nahiyar Afrika karo na farko.

Shekaru ashirin da biyar ke nan da suka gabata da Bafana Bafana suka taba daukar kofin na nahiyar Afrika a tarihin kwallon kafar kasar duk da kasancewarta cikin manyan kasashe a nahiyar ta Afrika.

Kwararran masani a fannin wasan kwallon kafa a kasar Mark Gleeson ya ce wannan rana ta zamo abar kwatance ga kasar sai dai tun daga wance lokacin zuwa yanzu kasar ta gaza maimaita irin wannan tarihin.

Afrika ta kudu dai ta doke Tunisia da ci biyu da nema a wasan karshe a gasar ta cin kofin Afrika da aka fafata a shekarar ta 1996 a filin wasa na Soccer City dake a Afrikan ta kudu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!