Connect with us

Labarai

Fiye da mutane 1,000 sun kamu da cutar Amai da Gudawa a Kamaru

Published

on

Alƙaluman hukumar lafiya a Kamaru sun ce mutanen da suka harbu da cutar kwalara ko kuma Amai da Gudawa a sassan ƙasar ya haura dubu guda inda kawo yanzu cutar ta kashe mutane 28 bayan ɓullarta a tsakiyar watan Yuli.

 

Rahotonni sun bayyana cewa, tuni aka tsaurara matakai a asibitoci don taƙaita yaɗuwar cutar yayin da ake killace waɗanda ke ɗauke da cutar a wani yanayi da yau Talata aka samu sabbin kamuwa da cutar a asibitin yanki na Mora wanda a baya cutar bata isa ba.

 

A cibiyar kula da cutuka ta yankin na Mora mutane 25 zuwa yanzu aka samu sun kamu da wannan cuta ciki har da guda da cutar ta yi ajalinsa.

 

Jami’an lafiyar da ke cibiyar sun shaidawa manema labarai a kowacce rana akan samu mutum ɗaya zuwa biyu sabbin kamuwa da cutar, lamarin da ya tilasta musu tsaurara matakai.

 

Da taimakon ƙungiyar Likitocin ƙasa da ƙasa ta MSF ne yanzu haka ake hoɓɓasa wajen ganin an daƙile yaɗuwar wannan cuta a shiyyoyin Fotokol da Mada da kuma Makary baya ga Kolofata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!