Labarai
Fiye da mutane 1,000 sun kamu da cutar Amai da Gudawa a Kamaru

Alƙaluman hukumar lafiya a Kamaru sun ce mutanen da suka harbu da cutar kwalara ko kuma Amai da Gudawa a sassan ƙasar ya haura dubu guda inda kawo yanzu cutar ta kashe mutane 28 bayan ɓullarta a tsakiyar watan Yuli.
Rahotonni sun bayyana cewa, tuni aka tsaurara matakai a asibitoci don taƙaita yaɗuwar cutar yayin da ake killace waɗanda ke ɗauke da cutar a wani yanayi da yau Talata aka samu sabbin kamuwa da cutar a asibitin yanki na Mora wanda a baya cutar bata isa ba.
A cibiyar kula da cutuka ta yankin na Mora mutane 25 zuwa yanzu aka samu sun kamu da wannan cuta ciki har da guda da cutar ta yi ajalinsa.
Jami’an lafiyar da ke cibiyar sun shaidawa manema labarai a kowacce rana akan samu mutum ɗaya zuwa biyu sabbin kamuwa da cutar, lamarin da ya tilasta musu tsaurara matakai.
Da taimakon ƙungiyar Likitocin ƙasa da ƙasa ta MSF ne yanzu haka ake hoɓɓasa wajen ganin an daƙile yaɗuwar wannan cuta a shiyyoyin Fotokol da Mada da kuma Makary baya ga Kolofata.
You must be logged in to post a comment Login