Labarai
Shugaba Tinubu ya naɗa sabon Shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Mista Abel Olumuyiwa Enitan a matsayin sabon Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya.
Sanarwar ta ce Enitan zai fara aiki ne daga ranar 27 ga Agusta, 2026, inda zai maye gurbin Didi Esther Walson-Jack, wadda za ta yi ritaya bayan ta kai shekarun ritaya.
Enitan,ya shafe shekaru bakwai da watanni bakwai yana rike da mukamin Sakataren Din-din-din a Ma’aikatar Harkokin ‘Yan Sanda, Ma’aikatar Harkokin Jin Kai da kuma Ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa. A halin yanzu yana matsayin Sakataren Din-din-din a Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya.
Shugaba Tinubu ya yaba wa tsohuwar shugabar ma’aikatan gwamnatin tarayya, Didi Walson-Jack, bisa irin gudunmawar da ta bayar wajen kawo sauye-sauye da sabbin dabaru a aikin gwamnati.
Ya kuma umurci Enitan da ya ci gaba da inganta sauye-sauyen da ake yi, tare da tabbatar da ƙwarewa, gaskiya, riƙon amana da ingantaccen aiki a cikin ma’aikatan gwamnati.
You must be logged in to post a comment Login