Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Siyasa

Shugabannin Labour Party na jihohin kasar sun jaddada goyon baya ga Julius Abure

Published

on

Shugabannin jam’iyyar adawa ta Labor Party na jihohin sun jaddada goyon bayansu ga shugaban jam’iyyar Julius Abure da umurnin kotu ta dakatar a baya.

A wata sanarwa da shugaban kungiyar kwadago ta Nijeriya NLC Komred Joe Ajero, ya fitar mai dauke da sa hannun sa kungiyar wadda ita ce ke da mallakin jam’iyyar ta LP, ta ce, Abure ta sani a matsayin shugaba.

Tun biyo bayan umurnin kotu na dakatar da Abure, magoya baya da dama sun yi ta yin dafifi a shalkwatar jam’iyyar domin hana shi yin jagoranci.

Sai dai Shugabannin jihohin sun ce wadanda su ke adawa da Abure na halin dakatarwa ne kafin su dau matakin don haka ba su da hurumin yin hakan.

Shugabannin sun kara da cewa, ya kamata kowa ya jira har sai an kammla shari’a kafin kawo kowane korafi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!