Connect with us

Labarai

Sojoji da taimakon dakarun CJTF sun lalata sansanonin yan ta’adda a dajin Sambisa

Published

on

Dakarun rundunar sojin Najeriya tare da haɗin gwiwar ƙungiyar yan sa-kai ta CJTF sun lalata sansanonin ‘yan ta’adda a dajin Sambisa da ke ƙaramar hukumar Gwoza a jihar Borno.

 

Rahotanni sun ce an gudanar da farmakin ne karshen makon da ya gabata inda dakarun suka kutsa cikin wuraren da ake zargin ‘yan ta’addar ISWAP ke amfani da su a ƙauyukan Disa da Balangaje.

 

An ce ‘yan ta’addar sun tsere da zarar sun hango dakarun sojin, lamarin da ya bai wa jami’an damar rusa sansanoninsu da cibiyoyin adana kayan aiki da suke amfani da su.

 

Hukumomin soji sun bayyana cewa wannan farmaki na daga cikin matakan da ake ci gaba da ɗauka domin hana ‘yan ta’adda sake kafa sansanoni a dajin Sambisa. Sun kuma tabbatar da cewa babu wani soja da ya rasa ransa ko ya jikkata yayin aikin.

   

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!