Labarai
Tsagin Wike ya magantu kan wallafa yan takarar PDP da INEC ta yi

Bangaren jam’iyyar PDP da ke goyon bayan Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya ce wallafa sunayen ‘yan takararsa na shugaban ƙasa da na majalisun dokoki da Hukumar INEC ta yi ya tabbatar da cewa jam’iyyar ta shirya tsaf domin babban zaɓen shekarar 2027.
A cikin wata sanarwa, sakataren yaɗa labarai na bangaren jam’iyyar, Jungudo Mohammed, ya ce bayyana sunayen Sandy Onor a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa da Babangida Umar a matsayin mataimakinsa ya ƙaryata iƙirarin da ake yi cewa PDP ba za ta tsayar da ɗan takara ba.
Mohammed ya kuma gode wa INEC, ɓangaren shari’a da hukumomin tsaro kan gudanar da aikinsu bisa doka. Ya ce jam’iyyar za ta ci gaba da yunƙurin sasanta saɓani a cikin gida tare da maraba da tsofaffin da sababbin mambobin da suka shiga cikinta, yana mai cewa PDP na da burin samar wa ‘yan Najeriya ingantaccen shugabanci a zaɓen 2027.
You must be logged in to post a comment Login