Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

WHO ta kaddamar da kwamitin karta-kwana kan COVID-19

Published

on

Hukumar lafiya ta duniya WHO ta kaddamar da kwamitin kartakwana kan rarababa kayayyakin dakile cutar COVID19 na Majalisar dinkin duniya.

Babban daraktan hukumar Dr, Tedros Ghebreyesus ya sanar da hakan ta cikin sanarwar da ya sanya a shafin sa na Internet bayan kaddamar da kwamitin a birnin Geneva.

Dr, Tedros Ghebreyesus ya ce zai yi amfani da wannan damar wajen godewa babbban sakataren na Majalisar dinkin duniya Antonio Guterres saboda hada kan hukumomin Majalisar dinkin duniya wuri guda don bada gudunmawar su kan dakile cutar Corona a duniya.

A cewar sa a yau ne aka cika kwanaki 100 tun bayan da WHO aka sanar da ita kan bullar cutar ta COVID-19 a kasar China.

Babban darkatan ya kuma abun mamaki ne cikin kankanin lokaci duniya ta sauya kan wannan mumunan cutar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!