Labarai
Yan tada ƙayar bayan fafutukar ɓallewa a Kamaru sun ayyana dokar kulle

Mayaƙa masu fafutukar ɓallewa a kasar Kamaru sun ayyana dokar kulle na tsawon mako guda a yankunan biyu na ƙasar da ake amfani da harshen Ingilishi.
Matakin ya haifar da tsaiko yayin da ake fara sabuwar shekarar karatu, tare da taƙaita zirga-zirga a yankunan Arewa maso Yamma da Kudu maso Yamma.
A birnin Buea da ke yankin Kudu maso Yamma, jami’an tsaro sun bazu a kan tituna, yayin da suke gudanar da bincike gida-gida.
An kashe kimanin mutum 6,000 a rikicin da ya kwashe shekara 10 tsakanin gwamnatin Kamaru mai amfani da harshen Faransanci da ƴan aware masu magana da Ingilishi, waɗanda ke fafutukar kafa ƙasa mai cin gashin kanta.
You must be logged in to post a comment Login