Connect with us

Addini

Yau mabiya addinin Kirista ke bikin Kirsimeti

Published

on

Yau Jumu’a ashirin da biyar ga watan Disamba, rana ce da mabiya addinin Kirista a sassa daban-daban na duniya ke gudanar da bikin kirsimeti, domin murnar tunawa da ranar haihuwar Yesu Almasihu (Annabi Isah A.S).

A lokacin wannan biki, mabiya addinin Kirista kan gudanar da hidimomi na ibada cikin farin ciki.

A nan Najeriya ma gwamnatin tarayya ta bada hutu domin bikin wannan rana.

Freedom Radio ta halarci bikin a Cocin Ecwa bisharar Hausa da ke Kano.

Ga wasu cikin hotuna daga Cocin

A yayin bikin, mataimakin Fadan Cocin Rabaran Barau Isah ya ja hankalin al’umma kan su cire banbancin addini domin tabbatar da ci gaban Najeriya.

A cewarsa, jingine banbancin addini a tsakanin juna zai taimaka wajen kawo ƙarshen matsalar tsaro da ke addabar ƙasar.

Rabaran Barau ya yi kira ga mabiya addinin Kirista da su yi biyayya da matakan kariya daga cutar Korona a yayin bukukuwan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!