Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An janye wa Magu jami’an tsaron da ke bashi kariya

Published

on

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta janye jami’an tsaron da ke aiki a gidan dakataccen shugaban hukumar EFCC Ibrahim Magu da kuma wadanda ke bashi kariya.

Rahotanni sun ce an kuma kwashe dukkanin motocin da ke gidan Ibrahim Magun a unguwar Maitama da ke Abuja.

A ranar Litinin din da ta gabata ne jami’an tsaron farin kaya suka yiwa dakataccen shugaban hukumar na EFCC rakiya zuwa ofishinsu da ke Abuja, kuma daga lokacin ne ya fara bayyana gaban kwamitin bincike na fadar shugaban kasa sakamakon zargin aikata rashawa da ake masa.

Tun daga lokacin ne kuma aka cigaba da tsare Ibrahim Magun a birnin tarayya Abuja. Ko da yake a ranar Juma’a ce Magun ya nemi babban sufeton yan sandan Najeriya ya bayar da belinsa.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!