Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ba yanzu za a bude tashoshin jiragen kasa ba – gwamnatin tarayya

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce dole ne ayi amfani da matakan kariya kan cutar Covid-19 da zarar an bude tashoshin jiragen kasa.

Ministan sufuri Rotimi Amaechi ya ce babu wani fasinja da za a yarje masa shiga jirgin kasa matsawar, ya ki amfani da dokokin da aka gindaya da suka kunshi amfani da safar rufe hanci da baki.

Ministan wanda ya bayyana hakan a shafinsa na Twitter, ya ce ma’aikatarsa bata shirya bude tashosin jiragen kasa ba a nan kusa.

A makon jiya ne kwamitin fadar shugaban kasa kan annobar Covid-19 ya bayyana cewa za a bude tashohin jiragen kasa, da zarar an bawa filayen jiragen sama damar fara aiki.

Jami’in gudanarwa na kwamitin Sani Aliyu ya ce za a bude tashoshin jiragen kasa da zarar, an janye dokar hana shige da fice a jihohin Najeriya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!