Connect with us

Labarai

Borno: Ma’aikatan ƙananan hukumomi sun yi zanga-zangar lumana

Published

on

Ma’aikatan ƙananan hukumomi a jihar Borno sun gudanar da zanga-zanga a Maiduguri don nuna rashin jin daɗinsu kan rashin aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashi na N70,000 da aka amince da shi a Najeriya. 

Shugaban kungiyar kwadago na jihar, Yusuf Inuwa, ya ce ma’aikatan ƙananan hukumomi ne suka fi fuskantar matsin rayuwa saboda hauhawar farashin kaya, inda ya bayyana cewa albashinsu ba ya isa ko na mako ɗaya. 

Ya kuma ce duk da gwamnati ta fara biyan wasu rukuni kamar malamai da ma’aikatan lafiya, yawancin ma’aikatan ƙananan hukumomi har yanzu ba su shiga tsarin sabon albashin ba.

A baya, gwamnatin jihar Borno ta bayyana cewa akwai ƙalubale wajen aiwatar da sabon albashin saboda yawan ma’aikata a ƙananan hukumomi, inda aka ce kusan ma’aikata 90,000 ne ke aiki a ƙananan hukumomi 27 na jihar.

Gwamnatin ta ce wasu ƙananan hukumomi suna samun kasa da Naira miliyan 700 a wata, alhali suna buƙatar sama da Naira miliyan 778 don biyan sabon albashin, lamarin da ke haifar da matsala wajen aiwatar da tsarin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!