Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

CAF: An rage dakatarwar da aka yiwa Austin Oladapo

Published

on

Kwamitin daukaka a kan al’amuran wasannin gasar confederation Cup ta Afrika, ya ragewa kyaftin din kungiyar kwallon kafa ta Enyimba, Austin Oladapo dakatarwar da akai masa daga shiga dukkan al’amuran gasar daga shekara 1 zuwa watanni 6.

Hukumar kwallon kafa ta Afrika Caf a baya ta dakatar da dan wasan na tsahon shekara daya, dalilin da ya sanya kenan kungiyar ta shigar da kara gaban kwamitin haka yasa aka rage zuwa watanni 6.

Muna bukatar bayanin rashin kokarin ‘yan wasan Najeriya a Tokyo 2020-Reps

Ana karar dan wasan na Enyimba da yin gwajin annobar covid 19 ta Bogi.

Haka zalika bayan an dakatar dashi daga wasa dan wasan ya sake bugawa kungiyar wasa na 2 a gasar cin kofin zakarun nahiyar Afrikan a Nigeria.

Kwamitin ya kuma ce kungiyar za ta rubutowa jami’an kula da lafiya na hukumar takardar neman afuwa bisa karyata jami’in lafiya da dan wasan ya yi a gaban jama’a, wanda dan wasan ya ringa cewa jami’in bai san aikinsa ba.

A Ranar 4 ga watan Janairun shekara ta 2022 ne dan wasan zai dawo ci gaba da bugawa kungiyar ta Enyimba wasa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!