Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Covid 19: gwamnati bata bawa kamfanoni damar shigo da allurar rigakafi ba

Published

on

Gwamnatin Tarayya ta ce ba ta ba da izinin shigo da alluran rigakafin COVID-19 daga kamfanonin masu zaman kan su zuwa kasar nan ba.

Ministan Lafiya Dakta Osagie Ehanire ne ya bayyana hakan ne a yayin taron kwamitin kar-ta-kwana mai yaki da cutar corona wanda aka gudanar a birnin tarayya Abuja.

Ya ce, ba a ba da izinin shigo da alluran COVID-19 daga kamfanoni masu zaman kansu ba saboda rahotannin da ake samu na samar da alluran marasa inganci.

Da yake magana kan batun ingancin allurar rigakafin ta Astrazeneca kuwa ministan ya sake ba da tabbacin cewa alluran na da inganci kuma bata da wata illa ga wadanda aka yiwa a kasar nan.

Dakta Osagie Ehanire ya kuma ce, tuni shugaban kasa da mataimakinsa da sauran shugabannin kasa suka karbi allurar rigakafin kuma a yanzu haka suna cikin koshin lafiya.

A cewar sa tuni hukumar kula da inganci abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta samar da wata hanya da za a aike mata sako musamman ga wadanda suka karbi rigakafin corona suka suskanci matsala.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!