Connect with us

Labarai

Gwamnan Filato ya buƙaci a haɗa hannu don magance ayyukan ta’addanci

Published

on

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Mutfwang, ya yi kira ga dukkan hukumomin tsaro, shugabannin al’umma da sauran masu ruwa da tsaki da su haɗa kai domin fuskantar matsalar ta’addanci da sauran ƙalubalen tsaro da ke barazana ga zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.

Gwamnan ya bayyana cewa nasarar yaƙi da matsalolin tsaro ba za ta samu ba sai an samar da cikakkiyar haɗin gwiwa tsakanin gwamnati, hukumomin tsaro da al’umma, yana mai jaddada cewa tsaro nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa.

Ya ce lokaci ya yi da za a ƙarfafa musayar bayanan sirri, haɗa kai wajen tattara bayanai da kuma ɗaukar matakan gaggawa domin dakile ayyukan ’yan ta’adda da masu tayar da zaune tsaye kafin su kai ga cimma mugayen manufofinsu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!