Labaran Kano
Gwamnatin Kano ta ce ruwan famfo zai dawo cikin birni kafin ƙarshen shekara

Gwamnatin jihar Kano ta ce tana sa ran dawo da ruwan famfo a cikin birnin Kano kafin ƙarshen wannan shekara.
Kwamishinan Muhalli, Ruwa da Sauyin Yanayi na jihar, Dakta Dahiru Muhammad Hashim, ya bayyana hakan yayin wata ziyara da ya kai domin duba aikin gyaran tashoshin samar da ruwa na Challawa da Tamburawa.
Ya ce ana ci gaba da gyaran matatar ruwan Challawa da kuma rumbun ajiyar ruwa na Goron Dutse, tare da shirin fara gwajin tsarin samar da ruwa a wasu sassan birnin.
A cewar kwamishinan, aikin na gudana ne a matakai, saboda ba za a iya magance dukkan matsalolin da suka shafi samar da ruwan a lokaci guda ba.
Dakta Dahiru ya ce gwamnatin jihar za ta gyara muhimman kayan aikin da suka lalace, domin kauce wa sake fuskantar matsalar karancin ruwa bayan kammala gyaran.
Ya kuma ce gwamnati za ta ci gaba da sa ido kan aikin, tare da tabbatar da cewa hukumomi da masu ruwa da tsaki da ke da alhakin samar da ruwan sun gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.
Gwamnatin ta ce burinta shi ne ganin al’ummar Kano sun samu wadataccen ruwan famfo.
You must be logged in to post a comment Login